羅馬書 11 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

羅馬書 11:1-36

上帝不放棄以色列人

1這樣,難道上帝放棄了祂的子民嗎?當然沒有!因我自己也是以色列人,是亞伯拉罕的後裔,屬於便雅憫支派。 2上帝並沒有放棄祂預先揀選的子民。你們不知道聖經上有關以利亞先知的記載嗎?他在上帝面前控告以色列人,說: 3「主啊!他們殘殺你的先知,拆毀你的祭壇,只剩下我一個人,他們還要殺我。」 4上帝怎樣回答呢?祂說:「我為自己留下七千人,他們未曾跪拜巴力。」

5現在的情況也是一樣,上帝按照揀選的恩典留下了少數人。 6既然說是出於恩典,就不再基於行為,不然恩典就不再是恩典了。 7這該怎麼說呢?以色列人努力追求,卻一無所得,只有蒙揀選的人得到了,其他的人都變得頑固不化。 8正如聖經上說:

「上帝使他們至今心智昏迷,

眼睛看不見,耳朵聽不到。」

9大衛也說:

「願他們的宴席成為網羅、

陷阱、絆腳石,

給他們帶來報應;

10願他們眼目昏暗,

無法看見,

永遠彎腰駝背。」

11那麼,以色列人一失足就再也爬不起來了嗎?當然不是!恰好相反,因他們的過犯,救恩臨到了外族人,使他們心生嫉妒。 12如果他們的過犯給世界帶來了富足,他們的失敗給外族人帶來了富足,那麼,他們發憤回頭的時候豈不要帶來更大的祝福嗎?

外族人得救

13我有話要對你們外族人說,因為我是外族人的使徒,我尊重自己的職分, 14希望使我的骨肉同胞心生嫉妒,好使他們當中的一些人得救。 15如果他們被拋棄,人類便有機會與上帝和好,那麼,當他們被接納的時候,又將怎樣呢?豈不是要死而復生嗎? 16獻祭時所獻的那部分麵團如果聖潔,整團麵也聖潔;樹根如果聖潔,樹枝也聖潔。

17如果橄欖樹上有幾條枝子被折了下來,你這野橄欖枝被接了上去,得以汲取橄欖樹根供應的汁漿,你就不可向折下來的枝子誇口。 18你怎能誇口呢?要知道:不是你托住樹根,而是樹根托住你。 19你也許會說:「原來的枝子被折下來,是為了把我接上去。」 20不錯,他們因為不信被折了下來,而你因為信被接了上去,然而不要自高,要敬畏上帝。 21上帝既然沒有留下原來的枝子,也可以不留下你。 22可見,上帝既慈愛又嚴厲。祂對墮落的人是嚴厲的,對你卻是慈愛的。你要常常活在祂的愛中,不然你也會被砍下來。 23當然,如果以色列人不再頑固不信,必會重新被接上去,因為上帝能把他們重新接上。 24你這從野生的橄欖樹上砍下來的枝子,尚且可以違反自然,被接到好橄欖樹上,何況原來的枝子被接回到原來的樹上呢?

全以色列都要得救

25弟兄姊妹,我不願意你們對以下這奧祕一無所知,還自以為聰明。這奧祕就是:雖然有些以色列人的心剛硬,但等到外族人得救的數目滿了以後, 26以色列都要得救。正如聖經上說:「救主必從錫安出來,祂將除去雅各子孫的罪惡。 27那時我要除去他們的罪,這是我與他們所立的約。」

28就福音而論,他們成為上帝的仇敵是為了使你們得到福音;就上帝的揀選而論,因為他們祖先的緣故,他們仍是上帝所愛的。 29因為上帝絕不會收回祂的恩賜和呼召。 30你們從前不順服上帝,然而因為他們的不順服,你們現在反蒙了憐憫。 31同樣,他們現在不順服是為了使你們蒙憐憫,好使他們也蒙憐憫。 32因為上帝把世人都歸在不順服之列,是為了要憐憫世人。

頌讚上帝

33啊,上帝的智慧和知識多麼博大精深!

祂的判斷多麼難測!

祂的蹤跡多麼難尋!

34誰曾知道主的心意?

誰曾做過祂的謀士?

35誰曾給過祂,

等祂償還呢?

36因為萬物都源於祂,

倚靠祂,歸於祂。

願榮耀歸給祂,

直到永遠。阿們!

Hausa Contemporary Bible

Romawa 11:1-36

Ragowar Isra’ila

1To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin. 2Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce, 3“Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”11.3 1Sar 19.10,14? 4Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”11.4 1Sar 19.18 5Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri. 6In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.

7To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare, 8kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Allah ya ba su ruhun ruɗewa,

idanu don su kāsa gani,

da kuma kunnuwa don su kāsa ji,

har yă zuwa yau.”11.8 M Sh 29.4; Ish 29.10

9Dawuda kuma ya ce,

“Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko,

sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.

10Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani,

bayansu kuma yă tanƙware har abada.”11.10 Zab 69.22,23

Rassan aure

11Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi. 12Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!

13Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa, 14da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu. 15Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba? 16In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.

17In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan, 18kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka. 19To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.” 20Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro. 21Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.

22Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka. 23In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su. 24Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?

Dukan Isra’ila za su tsira

25Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin ’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika. 26Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Mai ceto zai zo daga Sihiyona;

zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.

27Wannan kuwa shi ne alkawarina da su

sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”11.27 Ish 59.20,21; Ish 27.9; Irm 31.33,34

28Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu, 29gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa. 30Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu, 31haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku. 32Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa.

Ɗaukakawa

33Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace!

Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike,

hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!

34“Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji?

Ko kuwa yă ba shi shawara?”11.34 Ish 40.13

35“Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu,

da Allah zai sāka masa?”11.35 Ayu 41.11

36Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance.

Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin.