以弗所書 4 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

以弗所書 4:1-32

信徒同屬一體

1所以,我這為主被囚禁的勸你們,既然蒙了上帝的呼召,就要過與所蒙的呼召相稱的生活。 2凡事要謙虛、溫柔、忍耐,用愛心互相寬容, 3以和平彼此聯結,竭力持守聖靈所賜的合一。 4正如你們蒙召後有同一個盼望,你們同屬一個身體,有同一位聖靈、 5同一位主、同一個信仰、同一種洗禮、 6同一位上帝,就是萬物之父。祂超越萬物,貫穿萬物,且在萬物之中。

7然而,我們各人都是按照基督所賜的分量領受恩典。 8因此聖經上說:

「祂升上高天時,

帶著許多俘虜,

將恩賜賞給眾人。」

9既然說「升上」,豈不表示祂曾經降到地上嗎? 10降下的是祂,升到諸天之上的也是祂,祂充滿萬物。 11祂賜恩讓一些人作使徒,一些人作先知,一些人作傳福音的,一些人作牧師和教師, 12為要裝備信徒,使他們各盡其職,建立基督的身體, 13直到我們對上帝的兒子有一致的信仰和認識,逐漸成熟,達到基督那樣完美的生命。 14這樣,我們就不再像小孩子,被各種異端邪說之風吹得飄來飄去,被人的陰謀詭計欺騙,隨波逐流。 15相反,我們說話要憑愛心堅持真理,在各方面都要追求長進,更像元首基督。 16整個身體靠祂巧妙地結合在一起,筋骨相連,彼此供應,使各部位各盡其職,身體便漸漸長大,在愛中建立起來。

新人新生命

17因此,我奉主的名鄭重地勸告各位,不要再像不信的外族人一樣過著心靈空虛的日子。 18他們因為愚昧無知,頑固不化,理智受到蒙蔽,與上帝所賜的生命隔絕了。 19他們喪盡天良,放縱情慾,沉溺於各種污穢的事。 20但基督絕不是這樣教導你們的。

21如果你們聽過祂的事,領受了祂的教誨,就是在祂裡面的真理, 22就應該與從前的生活方式一刀兩斷,脫去因私慾的迷惑而漸漸敗壞的舊人, 23洗心革面, 24穿上照著上帝形像所造的新人。這新人有從真理而來的公義和聖潔。

25所以不要再說謊,大家都要彼此說真話,因為我們都是一個身體的肢體。 26不要因生氣而犯罪,不要到日落時還怒氣未消, 27不要讓魔鬼有機可乘。 28從前偷竊的要改過自新,自食其力,做正當事,以便能夠分給有需要的人。 29污言穢語一句都不可出口,要隨時隨地說造就人的好話,使聽的人得益處。 30不要讓上帝的聖靈擔憂,你們已經蓋上了聖靈的印記,將來必蒙救贖。 31要從你們當中除掉一切的苦毒、惱恨、怒氣、爭吵、毀謗和邪惡。 32總要以恩慈、憐憫的心彼此相待,要互相饒恕,正如上帝在基督裡饒恕了你們一樣。

Hausa Contemporary Bible

Afisawa 4:1-32

Tarayya a cikin jikin Kiristi

1A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku. 2Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna. 3Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna. 4Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku. 5Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya, 6Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.

7Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba. 8Shi ya sa aka4.8 Ko kuwa Allah ce,

“Sa’ad da ya hau sama,

ya bi da kamammu kamar tawagarsa

ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”4.8 Zab 68.18

9(Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba? 10Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.) 11Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai. 12Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi. 13Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.

14An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya. 15Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan 16dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.

Yin rayuwa kamar ’ya’yan haske

17To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani. 18Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu. 19Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.

20Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi. 21Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu, 22sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku. 23A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku. 24Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.

25Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne. 26“Cikin fushinku kada ku yi zunubi.”4.26 Zab 4.4 Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi, 27kada kuma ku ba wa Iblis dama. 28Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.

29Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta. 30Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa. 31Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta. 32Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.