马太福音 8 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

马太福音 8:1-34

麻风病痊愈

1耶稣下山的时候,有许多人跟着。 2有一个患麻风病的人跑来跪在祂跟前,说:“主啊,如果你肯,一定能使我洁净。”

3耶稣伸手摸他,说:“我肯,你洁净了吧!”那人的麻风病就立刻洁净了。

4耶稣对他说:“不要把这事告诉别人,要去让祭司察看你的身体,并且照摩西的规定献祭,向众人证明你已经洁净了。”

百夫长的信心

5耶稣到了迦百农,一个百夫长前来向祂求助,说: 6“主啊,我的仆人瘫痪,躺在家里,非常痛苦。”

7耶稣说:“我这就去医治他。”

8百夫长说:“主啊,我不配让你亲自来我家。你只要说一句话,我仆人就会痊愈。 9因为我有上司,也有部下。我命令我的部下去,他就去;要他来,他就来。我吩咐仆人做什么事,他一定照办。”

10耶稣听了,感到惊奇,便对跟随祂的人说:“我实在告诉你们,我在以色列从未见过信心这么大的人。 11我告诉你们,将来有许多从东从西来的人会在天国与亚伯拉罕以撒雅各一同欢宴。 12但那些本应承受天国的人反会被赶出去,在黑暗里哀哭切齿。”

13耶稣对百夫长说:“你回去吧!就照你所信的给你成就。”就在那时候,他的仆人便痊愈了。

治病赶鬼

14耶稣来到彼得家,看见彼得的岳母正在发烧,躺在床上。 15耶稣一摸她的手,烧就退了。她便起来服侍耶稣。

16当天晚上,有人带着许多被鬼附身的人来见耶稣。耶稣一句话就把鬼赶出去了,并医好了所有的病人。 17这是要应验以赛亚先知的话:“祂担当了我们的软弱,背负了我们的疾病。”

跟从耶稣的代价

18耶稣看到人群围着祂,就吩咐门徒渡到湖对岸。 19这时,有一位律法教师上前对耶稣说:“老师,无论你往哪里去,我都要跟从你。”

20耶稣说:“狐狸有洞,飞鸟有窝,人子却没有安枕之处。”

21另一个门徒对耶稣说:“主啊,请让我先回去安葬我的父亲。” 22耶稣对他说:“跟从我,让死人去埋葬他们的死人吧!”

平静风浪

23耶稣上了船,门徒也跟着祂上了船。 24忽然,湖面上狂风大作,波涛汹涌,船快要被巨浪吞没,耶稣却在睡觉。

25门徒连忙叫醒耶稣,说:“主啊,救命!我们快淹死了!”

26耶稣答道:“你们的信心太小了,为什么害怕呢?”于是祂起来斥责风和浪,风浪就完全平静了。

27门徒很惊奇,说:“祂究竟是什么人?连风浪都听祂的!”

治好两个被鬼附身的人

28耶稣到了对岸加大拉8:28 加大拉”即格拉森地区。人的地方,有两个被鬼附身的人从坟地里出来见祂。他们非常凶恶,没有人敢从那里经过。 29他们喊着说:“上帝的儿子啊!我们和你有什么关系?时候还没有到,你就来叫我们受苦吗?”

30当时,有一大群猪在附近吃食。 31鬼就哀求耶稣:“如果你要赶我们出去,就让我们进入猪群吧!”

32耶稣说:“去吧!”

于是,鬼从那二人身上出来,进入猪群,整群猪就一路奔下陡坡,冲进湖里淹死了。 33放猪的人逃进城,把事情的经过以及被鬼附身者的遭遇告诉了城里的人。 34于是,全城的人都出来见耶稣,见到后,便请求祂离开那地方。

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 8:1-34

Mutum mai kuturta

(Markus 1.40-45; Luka 5.12-16)

1Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi. 2Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”

3Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar8.3 Girik aka tsabtacce da shi daga kuturtarsa. 4Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”

Bangaskiyar jarumi

(Luka 7.1-10; Yohanna 4.43-54)

5Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako. 6Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”

7Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”

8Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke. 9Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”

10Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba. 11Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama. 12Amma za a jefar da ’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”

13Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.

Yesu ya warkar da mutane da yawa

(Markus 1.29-34; Luka 4.38-41)

14Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi. 15Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.

16Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya. 17Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

“Ya ɗebi rashin lafiyarmu,

ya kuma ɗauki cututtukanmu.”8.17 Ish 53.4

Wahalar bin Yesu

(Luka 9.57-62)

18Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin. 19Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”

20Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”

21Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”

22Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”

Yesu ya kwantar da hadari

(Markus 4.35-41; Luka 8.22-25)

23Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi. 24Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci. 25Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”

26Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.

27Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”

Warkar da mutum biyu masu aljanu

(Markus 5.1-20; Luka 8.26-39)

28Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa8.28 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Gergesenawa; waɗansu kuma Gerasenawa ne a nan (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya. 29Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?

30Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo. 31Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”

32Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa. 33Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu. 34Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.