路加福音 4 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

路加福音 4:1-44

耶稣受试探

1耶稣被圣灵充满,从约旦河回来后,随圣灵的引导来到旷野, 2在那里受魔鬼的试探四十天。那些日子耶稣什么也没吃。那段日子过后,祂饿了。 3魔鬼对祂说:“如果你是上帝的儿子,可以把这块石头变成食物来吃啊。”

4耶稣回答说:“圣经上说,‘人活着不是单靠食物。’”

5魔鬼又带祂上到高处,顷刻间把天下万国展示给祂看, 6又说:“我要把这一切权势和荣耀都给你,因为这一切全交给我了,我想给谁就给谁。 7所以如果你向我下拜,这一切就是你的了。”

8耶稣回答说:“圣经上说,‘要敬拜主——你的上帝,单单事奉祂。’”

9魔鬼又带耶稣到耶路撒冷,让祂站在圣殿的最高处,说:“如果你是上帝的儿子,就从这里跳下去吧, 10因为圣经上说,‘上帝会吩咐祂的天使保护你, 11他们会用手托住你,不让你的脚碰在石头上。’”

12耶稣回答说:“圣经上说,‘不可试探主——你的上帝。’”

13魔鬼用尽各样的试探后,暂时离开了耶稣。

拿撒勒人厌弃耶稣

14耶稣带着圣灵的能力回到加利利,祂的名声传遍了周围地区。 15祂在各会堂里教导人,大家都称赞祂。

16祂来到自己长大的地方拿撒勒,照常在安息日进会堂,并站起来诵读圣经。 17有人把以赛亚先知书递给祂,祂打开书卷,找到这样一段经文:

18“主的灵在我身上,

因为祂膏立了我,

让我传福音给贫穷的人,

差遣我宣告被掳的人得释放、

瞎眼的人得见光明、

受欺压的人得自由,

19又宣告上帝悦纳人的恩年已经来临。”

20耶稣读完便收好书卷,还给负责的人,然后坐下。会堂里的人都把目光集中在祂身上。

21祂就对他们说:“你们刚才听见的这段经文今天已经应验了。”

22大家都称赞祂,听见祂那些充满恩典的话,都感到惊奇,就说:“这不是约瑟的儿子吗?”

23耶稣对他们说:“你们肯定会把这句俗话用在我身上,说,‘医生啊,治好你自己吧!你在迦百农所行的一切,我们都听说了,也在你家乡行给我们看吧!’ 24可是我实在告诉你们,先知在自己的家乡都是不受欢迎的。 25事实上,在以利亚先知的时代,天干旱无雨达三年半之久,遍地有大饥荒。那时,以色列国有许多寡妇, 26以利亚并没有奉命去帮助她们任何人,只奉命去帮助住在西顿地区撒勒法的一个寡妇。 27以利沙先知的时代,以色列国有许多患麻风病的人,但没有一个人得到医治,反而叙利亚乃缦得到了医治。”

28会堂里的人听了这些话都怒火中烧, 29就起来把耶稣赶出城外,带到悬崖边,要把祂推下去。他们的城就坐落在山上。 30耶稣却从他们中间穿过,离开了那里。

加利利赶鬼医病

31耶稣下到加利利迦百农镇,在安息日教导众人。 32听众对祂的教导感到惊奇,因为祂的话里充满权柄。

33在会堂里有一个被污鬼附身的人高声喊叫: 34“唉!拿撒勒的耶稣啊,我们和你有什么关系?你是来毁灭我们吗?我知道你是谁,你是上帝的圣者!”

35耶稣责备它说:“住口!从他身上出来!”污鬼当场把那人摔倒,然后从他身上离开了,丝毫没有伤害他。

36大家都很惊讶,彼此议论说:“这是怎么回事?祂的话竟然带着权柄和能力,一吩咐污鬼,它们就出来了!”

37耶稣的名声传遍了周围地区。

耶稣医治许多人

38祂离开会堂,到了西门的家。那时,西门的岳母正在发高烧,众人就求耶稣医治她。

39耶稣站在她旁边,斥责热病,热病就退了,她便立刻起来服侍他们。

40到了黄昏,人们把患各种疾病的人带到耶稣面前。耶稣把手按在病人身上,一一治好他们, 41并赶出许多附在人身上的鬼。那些鬼喊叫着:“你是上帝的儿子!”耶稣却斥责它们,不许它们说话,因为它们知道祂是基督。

42黎明时,耶稣退到一处僻静的地方。众人四处找祂,找到后想留住祂,不让祂离开。 43但耶稣对他们说:“我必须把上帝国的福音传到其他的城镇去,因为我是为此而被差来的。” 44于是耶稣继续在加利利4:44 加利利”另有抄本作“犹太”。各会堂里传道。

Hausa Contemporary Bible

Luka 4:1-44

Gwajin Yesu

(Mattiyu 4.1-11; Markus 1.12,13)

1Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada, 2inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.

3Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”

4Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’4.4 M Sh 8.3

5Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya. 6Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama. 7Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”

8Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’4.8 M Sh 6.13

9Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa. 10Gama a rubuce yake,

“ ‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai,

su kiyaye ka da kyau;

11za su tallafe ka da hannuwansu,

don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’4.11 Zab 91.1,12

12Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’4.12 M Sh 6.16

13Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.

An ƙi Yesu a Nazaret

(Mattiyu 4.12-17; Markus 1.14,15)

14Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka. 15Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.

(Mattiyu 13.53-58; Markus 6.1-6)

16Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu. 17Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,

18“Ruhun Ubangiji yana kaina,

domin ya shafe ni,

in yi wa matalauta wa’azin bishara.

Ya aiko ni in yi shelar ’yanci ga ’yan kurkuku,

in kuma buɗe idanun makafi,

in ba da ’yanci ga waɗanda aka danne.

19In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”4.19 Ish 61.1 2

20Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa. 21Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”

22Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”

23Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’ ”

24Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa. 25Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar. 26Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon. 27Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”

28Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan. 29Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa, 30amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.

Yesu ya fitar da mugun ruhu

(Markus 1.21-28)

31Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane. 32Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.

33A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, 34“Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”

35Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.

36Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!” 37Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.

Yesu ya warkar da mutane da yawa

(Mattiyu 8.14-17; Markus 1.29-34)

38Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta. 39Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.

40Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su. 41Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.4.41 Ko kuwa Almasihu

42Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu. 43Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.” 44Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.