约翰福音 17 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

约翰福音 17:1-26

耶稣的祷告

1耶稣说完后,就抬头望着天说:“父啊!时候到了,愿你使你的儿子得荣耀,好让你的儿子也使你得荣耀。 2因为你把管理世人的权柄赐给了祂,使祂可以将永生赐予你交托给祂的人。 3这永生就是,认识你——独一的真神,并且认识你所差来的耶稣基督。 4我已经完成你交给我的工作,使你在地上得了荣耀。 5父啊,现在让我和你同享创世以前我们所共有的荣耀吧!

6“你从世上赐给我的人,我已将你17:6 ”希腊文是“你的名”,“名”代表一个人的全部。显明给他们。他们本来属于你,你将他们赐给了我,他们遵守你的道。 7如今他们知道,你赐给我的一切都是从你那里来的, 8因为我已经把你赐给我的道赐给他们,他们也接受了,并且确实知道我是从你那里来的,也相信是你差遣了我。

9“我不为世人祈求,却为他们祈求,就是为你赐给我的那些人祈求,因为他们属于你。 10一切属于我的都是你的,属于你的也是我的,我从他们身上得了荣耀。 11现在我要离开这个世界去你那里了,他们却仍然留在世上。圣父啊,求你为了自己的名,就是你赐给我的名而保守他们,使他们像我们一样合而为一。 12我和他们在一起的时候,靠着你赐给我的名保守他们,看顾他们。除了那个注定灭亡的人以外,他们一个也没有灭亡,这是为了应验圣经上的话。

13“现在我要去你那里了,我趁着还在世上的时候这样说,是要叫他们心里充满我的喜乐。 14我已将你的道赐给他们,世人恨他们,因为他们像我一样不属于这个世界。 15我不求你带他们离开这个世界,但求你保守他们脱离那恶者。 16因为他们像我一样不属于这个世界。 17求你用真理,就是你的道,使他们圣洁。 18你怎样差我到世上来,我也照样差他们到世人中间。 19为了他们,我献上自己,使他们借着真理可以圣洁。

20“我不但为这些人祈求,也为那些因他们的话而信我的人祈求, 21使他们都合而为一,正如父你在我里面,我在你里面一样,并且使他们也在我们里面,好让世人相信是你差我来的。 22我又将你赐给我的荣耀赐给他们,使他们像我们一样合而为一。 23我在他们里面,你在我里面,好使他们也完完全全地合而为一。这样,世人便知道我是你差来的,而且知道你爱他们,就像爱我一样。

24“父啊!我在哪里,愿你赐给我的人也在哪里,好让他们看见你赐给我的荣耀,因为在创世以前你已经爱我了。 25公义的父啊!世界还未认识你以前,我已经认识你了,这些人也知道是你差我来的。 26我使他们认识了你的名,我还要使他们更认识你,好让你对我的爱存在他们里面,我也在他们里面。”

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 17:1-26

Yesu ya yi addu’a

1Bayan da Yesu ya faɗi wannan, sai ya dubi sama ya yi addu’a ya ce,

“Uba, lokaci ya yi. Ka ɗaukaka Ɗanka, don Ɗanka yă ɗaukaka ka. 2Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. 3Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. 4Na ɗaukaka ka a duniya ta wurin gama aikin da ka ba ni. 5Yanzu ya Uba, ka ɗaukaka ni a gabanka da ɗaukakar da dā nake da ita tun kafin a kafa duniya.

Yesu ya yi addu’a saboda almajiransa

6“Na bayyana ka ga waɗanda ka ba ni a duniya. Su naka ne; kai ka ba ni su sun kuma yi biyayya da maganarka. 7Yanzu sun san cewa duk abin da ka ba ni daga gare ka ya fito. 8Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni. 9Ina addu’a dominsu. Ba domin duniya nake addu’a ba, amma domin waɗanda ka ba ni, gama su naka ne. 10Duk abin da nake da shi naka ne, kuma duk abin da kake da shi nawa ne. Na kuwa sami ɗaukaka ta wurinsu. 11Ba sauran zamana a duniya, amma waɗannan a duniya suke, ni kuwa ina zuwa wurinka. Ya Uba Mai Tsarki, ka kiyaye su ta wurin ikon sunanka, sunan da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya. 12Yayinda nake tare da su, na kāre su na kuma kiyaye su ta wurin sunan nan da ka ba ni. Ba ko ɗayan da ya ɓace, sai dai wannan da aka ƙaddara zuwa ga hallaka don Nassi yă cika.

13“Yanzu ina zuwa wurinka, sai dai na faɗi waɗannan abubuwa ne tun ina a duniya domin farin ciki yă zama cikakke a cikinsu. 14Na gaya musu maganarka duniya kuwa ta ƙi su, don su ba na duniya ba ne yadda ni ma ba na duniya ba ne. 15Ba addu’ata ba ce ka ɗauke su daga duniya ba, sai dai ka kāre su daga mugun nan. 16Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne. 17Ka tsarkake su ta wurin gaskiya; maganarka ce gaskiya. 18Kamar yadda ka aiko ni cikin duniya, haka ni ma na aike su cikin duniya. 19Saboda su ne na tsarkake kaina, domin su ma a tsarkake su da gaske.

Yesu ya yi addu’a saboda dukan masu bi

20“Addu’ata ba saboda masu bina kaɗai ba ne. Ina addu’a kuma saboda waɗanda za su gaskata da ni ta wurin maganarsu. 21Ina so dukansu su zama ɗaya, ya Uba, kamar yadda kake a cikina, ni kuwa a cikinka. Haka su ma bari su zauna cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa kai ka aiko ni. 22Na ba su ɗaukakar da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya. 23Ni a cikinsu kai kuma a cikina. Bari su kasance da cikakken haɗinkai, domin duniya ta san cewa kai ka aiko ni. Ka kuwa ƙaunace su yadda ka ƙaunace ni.

24“Uba, ina so waɗanda ka ba ni su kasance tare da ni a inda nake, su kuma ga ɗaukakata, ɗaukakar da ka ba ni domin kana ƙaunata kafin halittar duniya.

25“Ya Uba Mai Adalci, ko da yake duniya ba tă san ka ba, ni na san ka, sun kuma san kai ka aiko ni. 26Na bayyana ka a gare su, zan kuma ci gaba da bayyana ka domin ƙaunar da ka yi mini ta kasance a cikinsu ni ma in kasance a cikinsu.”