约翰福音 16 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

约翰福音 16:1-33

圣灵的工作

1“我把这些事告诉你们,以免你们失去信心。 2人们将把你们赶出会堂,时候将到,杀害你们的人还以为是在事奉上帝。 3他们这样做,是因为他们根本不认识父,也不认识我。 4我把这些事提前告诉你们,是要叫你们到时候可以想起我曾跟你们讲过这些事。我以前没有告诉你们,那是因为我还跟你们在一起。

5“现在我要去差我来的父那里,你们没有人问我去哪里。 6因为我把这些事告诉了你们,你们心里充满了忧愁。 7然而,我把实情告诉你们,我去对你们是有益的,因为如果我不去,护慰者就不会来,我去了就会派祂到你们这里来。 8祂来了,就要在罪、义、审判方面责备世人。 9在罪方面责备他们,是因为他们不信我; 10在义方面责备他们,是因为我要去父那里,你们再也看不到我了; 11在审判方面责备他们,是因为这世界的王受了审判。

12“我还有许多事情要告诉你们,可是你们现在不能明白。 13等到真理之灵来了,祂会引导你们,让你们明白一切的真理。祂不凭自己说话,而是把祂所听见的和有关将来的事告诉你们。 14祂也要把从我那里领受的指示你们,使我得荣耀。 15因为父的一切都是我的,所以我才说祂要把从我那里领受的指示你们。

转忧为喜

16“不久,你们就见不到我了,再过不久,你们还会看见我。”

17几个门徒彼此议论说:“祂说,‘不久,你们就见不到我了,再过不久,你们还会看见我’,祂又说,‘因为我要去父那里’,这到底是什么意思呢? 18祂说‘不久’是什么意思呢?我们真不明白!”

19耶稣知道他们想问祂,就说:“你们在议论我刚才说的话是什么意思吗? 20我实实在在地告诉你们,你们将痛哭、哀号,世人却要欢喜;你们将忧愁,然而你们的忧愁将变为喜乐。 21妇人分娩时都会痛苦不已,但孩子生下来后,她就会因为这世界添了一个新生命而充满欢乐,忘掉了生产的痛苦。 22同样,现在你们有忧愁,但到我再见你们的时候,你们的心必欢喜,而且这份喜乐是谁也夺不去的。

23“到那一天,你们就什么也不用问我了。我实实在在地告诉你们,你们奉我的名无论向父求什么,祂都会赐给你们。 24你们从来没有奉我的名求过什么,你们现在求,就必得到,好使你们的喜乐满溢。

胜过世界

25“我一直用比喻跟你们讲这些事,不久,我就不再用比喻了,而是清楚地把父的事告诉你们。 26到那天,你们将要奉我的名祈求,我不是说我要为你们向父祈求。 27父爱你们,因为你们一直爱我,并且相信我来自上帝。 28我从父那里来到这个世界,现在我要离开这个世界回到父那里。”

29门徒说:“如今你直截了当地告诉我们,不再用比喻了。 30现在我们知道你无所不知,无需人向你发问,因此我们相信你来自上帝。”

31耶稣说:“你们现在相信吗? 32看啊!时候快到了,现在就是,你们将要分散,各自回家,只留下我一人。不过,我并非一人,因为父与我在一起。 33我把这些事告诉你们,是要叫你们在我里面有平安。你们在世上会有苦难,但你们要放心,我已经胜过这个世界。”

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 16:1-33

1“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe. 2Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne. 3Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba. 4Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.

Aikin Ruhu Mai Tsarki

5“Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’ 6Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki. 7Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku. 8Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci, 9a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba; 10a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba; 11a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.

12“Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba. 13Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna. 14Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku. 15Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’ ”

Baƙin cikin almajirai zai koma farin ciki

16Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”

17A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?” 18Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”

19Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’? 20Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki. 21Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya. 22Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku. 23A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana. 24Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.

25“Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana. 26A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba. 27Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito. 28Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”

29Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba. 30Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”

31Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata! 32Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.

33“Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”