约翰一书 5 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

约翰一书 5:1-21

胜过世界的人

1每一个信耶稣是基督的人,都是从上帝生的。凡爱生他之上帝的,也爱上帝所生的。 2当我们爱上帝,遵行祂的命令时,便知道自己也爱祂的儿女。 3因为我们遵行上帝的命令就是爱上帝,祂的命令并不难遵守。 4因为凡是从上帝生的人都能胜过世界,使我们得胜的是我们的信心。 5谁能胜过世界呢?不就是那些信耶稣是上帝的儿子的人吗?

上帝的见证

6耶稣基督是借着水和血来的。祂不单是借着水来的,也是借着水和血来的,并且有圣灵为祂做见证,圣灵就是真理。 7这样,做见证的共有三样: 8圣灵、水和血。这三者是一致的。 9我们既然接受人的见证,就更该接受上帝的见证,因为上帝为祂的儿子做了见证。 10信上帝儿子的人心里有这见证,不信上帝的人等于把上帝当作撒谎的,因为他不信上帝为祂儿子做的见证。 11这见证就是:上帝已经把永恒的生命赐给我们,这生命在祂儿子里面。 12人有上帝的儿子,就有这生命;没有上帝的儿子,就没有这生命。

永恒的生命

13我把这些事写给你们这些信上帝儿子之名的人,是要你们知道自己有永生。 14我们若按着上帝的旨意祈求,祂必垂听,这是我们对上帝的信心。 15我们既然知道上帝垂听我们一切的祈求,就知道我们能得到所求的。

16若有人看见信徒犯了不至于死的罪,就当为他祷告,上帝必将生命赐给他。有的罪会导致死亡,我并不是说你们要为这样的罪祷告。 17一切不义的事都是罪,但有的罪不会导致死亡。

18我们知道从上帝生的不会继续犯罪,因为上帝的儿子保护他,那恶者无法害他。 19我们知道自己属于上帝,全世界都在那恶者手中。

20我们知道上帝的儿子已经来了,并且赐给了我们悟性,使我们能认识真神。我们在真神里面,就是在祂儿子耶稣基督里面。祂是真神,也是永生。

21孩子们啊,你们要远离偶像!

Hausa Contemporary Bible

1 Yohanna 5:1-21

Bangaskiya cikin Ɗan Allah

1Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma. 2Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar ’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa. 3Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne; 4domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya. 5Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.

6Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya. 7Akwai shaidu uku, wato, 8Ruhu,5.7,8 Rubuce-rubucen hannu na baya-bayan nan na Bulget shaida a sama: Uba, Kalma da kuma Ruhu Mai Tsarki, waɗannan uku kuwa ɗaya ne. 8 Akwai kuma uku da suka ba da shaida a duniya, wannan: Ruhu (babu kalman nan a rubuce-rubucen hannu na Girik kafin karni na goma sha shida) da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce. 9Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa. 10Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba. 11Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. 12Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.

Ƙarshen magana

13Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. 14Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu. 15In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.

16Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba. 17Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.

18Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba. 19Mun san cewa mu ’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun. 20Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada.

21’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.