希伯来书 3 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

希伯来书 3:1-19

耶稣超越摩西

1因此,同蒙天召的圣洁的弟兄姊妹,你们应当仔细思想那位我们公认为特使和大祭司的耶稣。 2祂向委任祂的上帝尽忠,就好像摩西向上帝的全家尽忠一样。 3然而祂却比摩西配得更大的荣耀,因为建造房子的人当然比房子更尊贵。 4所有的房子都有建造者,但建造万物的是上帝。 5摩西以仆人的身份向上帝的全家尽忠,为将来要宣告的事做见证。 6但基督是以儿子的身份忠心治理上帝的家。我们若坚强勇敢,持定引以为荣的盼望,我们就是祂的家了。

不可存刚硬的心

7因此,正如圣灵说:

“你们今天若听见祂的声音,

8不可心里顽固,

像从前在旷野试探祂、悖逆祂一样。

9当时,你们的祖先试我、探我,

观看我的作为达四十年之久。

10所以,我向那世代的人发怒,

说,‘他们总是执迷不悟,

不认识我的道路。’

11我就在愤怒中起誓说,

‘他们绝不可进入我的安息。’”

12弟兄姊妹,要谨慎,免得你们当中有人心存恶念,不肯相信,背弃了永活的上帝。 13趁着还有今日,要天天互相劝勉,免得有人被罪迷惑,心里变得刚硬。 14如果我们将起初的信念坚持到底,便在基督里有份了。

15圣经上说:

“你们今日若听见祂的声音,

不可像从前那样硬着心悖逆祂。”

16听见祂的声音却又悖逆祂的是谁呢?不就是摩西埃及领出来的那些人吗? 17四十年之久惹上帝发怒的是谁呢?不就是那些犯罪作恶并倒毙在旷野的人吗? 18上帝起誓不准谁进入祂的安息呢?不就是那些不肯信从的人吗? 19可见,他们不能进入上帝的安息是因为不信的缘故。

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 3:1-19

Yesu ya fi Musa

1Saboda haka, ’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa. 2Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah. 3An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja. 4Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne. 5Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba. 6Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.

Gargaɗi a kan rashin bangaskiya

7Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce,

“Yau, in kuka ji muryarsa,

8kada ku taurare zukatanku,

yadda kuka yi a tawayen nan,

a lokacin gwaji a hamada,

9inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni,

ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.

10Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani,

na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke,

ba su kuma san hanyoyina ba.’

11Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina,

‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’ ”3.11 Zab 95.7-11

12Ku lura fa, ’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai. 13Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi. 14Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe. 15Kamar yadda aka faɗa cewa,

“Yau, in kuka ji muryarsa,

kada ku taurare zukatanku

kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”3.15 Zab 95.7,8

16Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba? 17Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba? 18Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba? 19Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.